Dakarun Tabbatar da zaman lafiya a kasar Afirka ta tsakiya sun sanar da mutuwar mutane 20 a sabon rikicin da ya barke a kasar.
Kamfanin Dillancin labarun Associated Press daga birnin Bongui ya ambato kwamandan dakarun tabbatar da zaman lafiya, Renar Onana yana cewa; A yankin Kaga-Bandoro an kashe mutane 20 da kuma jikkata wasu 41.
Kwamandan dakarun tabbatar da zaman lafiyar ya kara da cewa; Rikicin wanda ya barke a jiya alhamis ya faru ne a kusa da sansanin dakarun tabbatar da zaman lafiyar.
Duk da cewa an sami koma bayan tashe-tashen hankula a kasar sai dai jefi-jefi ana samun rikici.288